Location:

United States

Genres:

Podcasts

Networks:

RFI

Language:

English


Episodes
Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin masu sauraro kan matakin kasashen yammacin Afrika dake mafani da kudin CFA - 23/12/2019

12/22/2019
Shirin ra'ayoyin masu saurare ya tattauna kan matakin kasashen yammacin Afrika 8 renon Faransa, da suka amince da sauya sunan takardar kudin da suke amfani da ita a hukumance daga CFA zuwa Eco, a daidai lokacin da kungiyar kasashen yammacin Africa ke shirin samar da kudin bai - daya mai suna ECO, lamarin da ake ganin riga – malam masallaci ne ga shirin na ECOWAS.

Duration:00:15:23

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyi kan tasirin dakarun kasashen ketare wajen yakar ta'addanci a Sahel - 17/12/2019

12/16/2019
Taron shugabannin kasashe 5 na yankin Sahel da ya gudana ranar lahadi a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, ya jaddada muhimmancin ci gaba da hulda da kasashen duniya don yaki da ta’addancin a yankin na Sahel. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da, a wasu kasashe aka fara nuna shakku dangane da irin rawar da dakarun kasashen yammacin duniya ke takawa a wannan yaki. Menene ra’ayoyinku game da amfani ko rashin amfani dakarun kasashen ketare a wannan yaki? Anya yankin Sahel zai iya tabbatar...

Duration:00:14:47

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyi kan kashe jami'an kungiyar agajin Faransa da Boko Haram tayi - 16/12/2019

12/15/2019
Kungiyar agajin kasar Faransa ta Action Against Hunger ta sanar da kashe jami’an ta guda 4 da kungiyar Boko Haram tayi garkuwa da su tun a watan Yuli. Kisan ya gamu da suka daga Majalisar Dinkin Duniya da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da kuma kungiyar agajin dake taimakawa mutane 300,000 da rikicin Boko Haram ya tagayyara. Kan wannan batu muka baku damar tattaunawa a wannan litinin.

Duration:00:15:32

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyi kan batutuwa dake ciwa masu saurare tuwo a kwarya - 22/11/2019

11/21/2019
Shirin ra'ayoyin maso sauraro kowace Jumma'a na bada damar tofa albarkacin bakin kan duk wasu batutuwa da ke cimmuku tuwo a kwarya, a wannan karon ma masu saurararo sun bayyana ra'ayoyin su kan batutuwa da dama.

Duration:00:15:57

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyi kan ranar bandakuna ta duniya - 19/11/2019

11/18/2019
Shirin Ra'ayoyin Masu Sauraro na wannan ranar ya bada damar yin tsokaci ne kan ranar bandakuna ta duniya, ranar da ake karfafa wayar da kan jama'a kan yakar yin bahaya a bainar jama'a. Bikin na bana yazo ne yayinda majalisar dinkin duniya ta ce sama da mutane biliyan 3 ke rayuwa cikin rashin tsaftar muhalli.

Duration:00:15:06

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyi kan kudirin dokar hukunta masu yada kalaman kiyayya - 14/11/2019

11/13/2019
Majalisar dokokin Najeriya ta gabatar da kudirin dokar hukunta duk wanda aka kama da laifin yada kalaman kiyayya, da daurin shekaru 10 a gidan yari ko biyan tarar naira miliyan 10. Matakin ya haifar da suka daga bangarorin adawa, alkalai da kuma kungiyoyin fararen hula, inda suka ce kudurin dokar ya yi tsanani. Kan wannan al'amari a wannan karon muka baiwa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyi akai.

Duration:00:15:34

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyi kan rahoton da yace Najeriya ce kasa ta 2 a duniya da ake aurar yara mata - 12/11/2019

11/11/2019
Kamar yadda wata kila kuka ji a cikin labaran duniya, shugaban kasar Bolivia Evo Morales ya yi murabus daga mukaminsa sakamakon takkadamar da ta biyo bayan sake nasarar zabensa, wanda yasa sojan Kasar da ‘Yan sanda janye goyon baya da suke bashi. Gwamnatin Bolivia ta bayyana shirinta na sake gudanar da sabon zabe dan kawo karshen rikicin siyasar Kasar. Kan wannan batu muka baku damar tofa albarkacin baki, a wannan rana ta talata 12 ga Nuwamban 2019.

Duration:00:16:06

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin masu sauraro kan mutuwar Abubakar al-Baghdadi - 29/10/2019

10/28/2019
Kasashen duniya na ci gaba da bayyana farin ciki kan samun nasarar kashe shugaban kungiyar mayakan IS, Abubakar al-Baghadadi da dakarun Amurka suka yi saboda illar da ya yiwa duniya. Sama da Kasashe 30 dake yaki da kungiyar na shirin ganawa a ranar 14 ga watan nuwamba dan cigaba da neman Karin goyan baya daga abokan su wajen yaki da ta’addanci. Kan wannan batu muka baiwa masu sauraro damar tofa albarkacin bakinsu.

Duration:00:16:27

Ask host to enable sharing for playback control

Shugaba Biya na Kamaru ya fara daukan matakan sulhu da abokan hamayya - 07/10/2019

10/6/2019
A kokarinsa na sulhunta bangarorin kasar, shugaban Kamaru Paul Biya, ya saki jagoran adawar kasar Maurice Kamto da wasu magoya bayansa, da kuma wasu ‘yan aware da ke tsare a kurkuku, ba tare da ...

Duration:00:14:33

Ask host to enable sharing for playback control

Tattaunawa da ra'ayoyin masu saurare kan harajin ajiya ko cire kudi a bankunan Najeriya - 19/09/2019

9/18/2019
Ra'ayoyin masu sauraro na wannan rana tare da Zainab Ibrahim ya tattauna kan matakin babban bankin Najeriya CBN na karin harin masu ajiya da kuma fitar da kudin a bankunan kasar.

Duration:00:15:14

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin masu sauraro kan al'amuran da ke ci musu tuwo a kwarya - 12/07/2019

7/11/2019
Shirin Ra'ayoyin Masu Sauraro na wannan rana ta Juma'a, kamar yadda aka saba ya bada damar tattaunawa da jan hankalin hukumomi kan muhimman batutuwan da ke damun al'umma.

Duration:00:15:12

Ask host to enable sharing for playback control

Tattaunawa da ra'ayoyin masu saurare - 28/06/2019

6/27/2019
A kowace ranar Jumma'a shirin ra'ayoyin masu saurare kan baku damar tofa albarkacin bakin ku kan duk wani maudu'in da ke cimmu ku tuwo a kwarya.

Duration:00:14:38

Ask host to enable sharing for playback control

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta kara saka wasu yankunan kasar a cikin dokar ta baci - 04/12/2018

12/3/2018

Duration:00:16:08

Ask host to enable sharing for playback control

Za'a rufe tashoshin samar da makamashin nukiliyar 14 a Faransa nan da shekarar 2035. - 28/11/2018

11/27/2018
Shirin ra'ayoyin ku masu saurare na wannan ranar tare da Zainab Ibrahim, ya tattauna ne kan matakin shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron kan shirin rufe tashoshin samar da makamashin nukiliyar kasar 14 daga cikin 58 da suke da shi nan da shekarar 2035.

Duration:00:15:10

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin masu sauraro kan takaddamar neman karin albashi a Najeriya da kuma matakin shiga yajin aiki - 06/11/2018

11/5/2018
Kamar yadda watakila kuka ji a labaran duniya, bayan kwashe tsawon watanni na kokarin cimma yarjejeniya, yanzu haka Kungiyoyin Kwadagon Najeriya sun cimma matsaya da gwamnatin kasar kan mafi karancin albashin ma’aikata. Menene ra’ayoyinku kan tsawon lokacin da aka dauka na cece-kuce tsakanin bangarorin biyu kan wannan batu? Ko kuna ganin cewa, shugaba Buhari zai amince da dogon yajin aiki a dai dai lokacin da zabe ke karatowa? Shin kuna ganin yajin aiki na taka muhimmiyar rawa wajen...

Duration:00:15:15

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin masu sauraro kan Ranar Abinci ta Duniya - 16/10/2018

10/15/2018
Kowacce Ranar 16 ga watan Oktoba, rana ce da Majalisar Dinkin Duniya ke warewa a matsayin ranar samar da abinci ta duniya. Taken bikin na bana dake gudana a birnin Geneva shi ne ‘Ana iya magance yunwa a duniya.’ Shirin Ra'ayoyin ku masu sauraro na wannan lokaci, ya baku damar tofa albarkancin bakinku kan yadda harkar noma da samar da abinci ke gudana a yankunan ku.

Duration:00:15:28

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin masu sauraro kan zaben shugabancin kasar Kamaru - 09/10/2018

10/8/2018
Shirin Ra'ayoyin Masu Sauraro na wannan lokacin, ya bada damar tofa albarkacin baki ne kan dambarwa dake neman kunno kai a zaben kasar Kamaru, inda dan takara daga jam’iyyar adawa, Maurice Kamto ke ikirarin lashe zaben shugabancin kasar, gabanin fitar da sakamakon hukumar zabe. Sai dai gwamnatin kasar ta yi watsi da ikirarin na Kamto tare da jan kunnensa.

Duration:00:15:17

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin masu sauraro kan matsalar yajin aikin malaman makarantu a Jamhuriyar Nijar - 03/10/2018

10/2/2018
Kamar yadda wasu suka samu saurara a labarun duniya da sashin Hausa na RFI ya watsa, a makon jiya ne makarantun boko a Jamhuriar Nijar da suka hada da jami'o'i suka koma bakin aiki bayan janye yajin aikin da suka tsunduma. Matsalar yajin aiki na haifar da cikas ga bangaren ilimi a Nijar, lura da cewa kusan kowacce shekara sai malamai sun gudanar da ita. Shirin ra'ayoyin ku asu sauraro ya baku damar tofa albarkancin bakinku ne akan yadda za a shawo kan wannan matsala.

Duration:00:15:30

Ask host to enable sharing for playback control

Ra'ayoyin Masu sauraro kan zanga zangar kin jinin China a kasar Zambiya - 25/09/2018

9/24/2018
Ra'ayoyin masu saurare, kan sanin ko kasancewar kasar china a kasuwanin nahiyar Afrika wani sabon salon mulkin mallaka ne, ta hanyar damfarawa kasashen nahiyar bashi kamar yadda kasashen yammaci ...

Duration:00:15:22

Ask host to enable sharing for playback control

Majalisar dinkin duniya tace galibin makarantu a duniya basu da ruwan sha mai tsafta - 28/08/2018

8/27/2018
hukumar lafiya ta majalisar dinkin duniya ta ce yanzu haka rabin makarantun duniya basu da tsaftatacin ruwan sha, da kuma bandaki, tare da wajen wanke hannu.

Duration:00:15:45