Daga Laraba-logo

Daga Laraba

News & Politics Podcasts

Shiri ne da ke tattaunawa mai zurfi a kan batutuwan da suka shafi al'umma kai-tsaye, da nazari a kan tasirin da za su iya yi, da nemo hanyar magance ko kauce wa illolin da za su iya hifarwa bayan jin ta-bakin wadanda abin ya shafa.

Location:

Nigeria

Description:

Shiri ne da ke tattaunawa mai zurfi a kan batutuwan da suka shafi al'umma kai-tsaye, da nazari a kan tasirin da za su iya yi, da nemo hanyar magance ko kauce wa illolin da za su iya hifarwa bayan jin ta-bakin wadanda abin ya shafa.

Language:

Hausa

Contact:

08028788121


Episodes
Ask host to enable sharing for playback control

Dabarun Kauce Wa Dagulewar Lissafi Sakamakon Ruwan Sama

7/24/2024
A wannan yanayi na damina kusan kullum wuni ake yi ana tafka ruwan sama a wasu sassan Najeriya. Akwai masu sana’o’in da sai sun fita za a samu taro da sisi amma kuma babu hali. Shirin Daga Laraba zai tattauna lan dabarun da ya kamata masu sana’o’i su yi amfani da su domin ganin ruwan sama bai dagula musu lissafi ba.

Duration:00:23:21

Ask host to enable sharing for playback control

Ko Tallafin Shinkafar Gwamnati Zai Magance Damuwar Talakan Najeriya?

7/17/2024
Tun bayan janye tallafin man fetur, gwamnati ke ta rarraba kayan abinci ga talakawa domin rage musu radadi. A wannan makon Shugaban Kasa Bola Tinubu ya bayar da umarin raba tirela 20 ga kowace jiha a Najeriya da Birnin Tarayya duk da wasu na wannan salo ba ya tasiri. Shirin Daga Laraba ya duba yadda tallafin abincin daga gwamnatin zai magance damuwar talakan Najeriya.

Duration:00:24:56

Ask host to enable sharing for playback control

Matakan Kauce Wa Hadarin Ambaliyar Ruwa

7/10/2024
Kusan ko wace damina sai hukumomi sun gargadi mazauna wasu yankuna game da yiwuwar samun ambaliyar ruwa. A bana ma Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMET) ta yi gargadin cewa jihohi kusan 31 za su fuskanci ambaliyar da rushewar gine-gine. Shirin Daga Laraba ya tattauna kan abin da ya kamata a yi domin kauce wa asara sakamakon ambaliya.

Duration:00:29:48

Ask host to enable sharing for playback control

Digiri Ko Sana’a - Wanne Ya Fi Muhimmanci?

7/3/2024
Ana ci gaba da tafka muhawara a kan abin da ya kamata mutum ya fi bai wa muhimmanci a tsakanin digiri da sana’a. Shin wanne ne daga ciki mafi a'ala a rayuwar mutum? Shirin Daga Laraba zai yi muhawara a kan wannan batu.

Duration:00:29:50

Ask host to enable sharing for playback control

Shirin Gwamnonin Arewa Maso Yamma Na Magance Matsalar Tsaro

6/26/2024
Yayin da ake kammala taron yini biyu a kan matsalar tsaro a shiyyar Arewa maso yammacin Najeriya, hankali ya karkata zuwa ga mataki na gaba. Shirin Daga Laraba na wannan makon zai duba yadda gwamnonin yankin suka shirya aiwatar da abin da aka cimma.

Duration:00:23:01

Ask host to enable sharing for playback control

Yadda Kanawa Suka Je Kallon Hawan Daushe A Zazzau

6/19/2024
Hawan Daushe al’ada ce ta sarakunan Kasar Hausa a lokacin bikin Sallah. A masarautar Zazzau a kan yi wannan hawa a ranar ukun Sallah da yamma, kuma yakan tara ‘yan Kallo daga wurare daban-daban ciki har da Kano. Shirin Daga Laraba na wannan makon zai duba yadda aka yi hawan na bana da yadda ya samo asali musamman a masarautar Zazzau.

Duration:00:28:40

Ask host to enable sharing for playback control

‘Na Yi Nadamar Ajiye Aiki Saboda Tsohon Mijina’

6/12/2024
Yayin da wasu mazan suke kyale matansu su yi aiki, wasu kan yi kememe su ki bari nasu matan su yi. Shin barin matar aure ta yi aiki ne ya fi alheri ko hana ta? Wadanne dalilai kowanensu ke da su? Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba a cikin wannan lamari.

Duration:00:25:09

Ask host to enable sharing for playback control

Dalilin Da Maza Ba Su Son Likita Namiji Ya Duba Matansu

6/5/2024
A yanayi na rashin lafiya a kan ga wasu maza na tuburewa likita namiji ba zai duba musu iyali ba, musamman wajen haihuwa a asibitoci. Amma akwai matan da su ma a ganin su, kunya kan hana su sakin jiki likitoci maza su duba su. Shirin Daga Laraba na wannan makon ya yi nazari a kan meyasa wasu basu yarda likita namiji ya duba matansu a asibiti.

Duration:00:28:54

Ask host to enable sharing for playback control

Ƙalubale Da Ci Gaban Dimokraɗiyar Najeriya Cikin Shekara 25

5/29/2024
Najeriya ta cika shekara 25 cikin tsarin dimokradiyya ba tare da katsewa ba. Ana kan tsari ne na shugaban kasa mai cikakken iko tun daga 1999 a ranar 29 ga watan mayu, duk da yake an sauya bikin wannann rana zuwa 12 ga watan Yuni. Toh shin wane irin ci gaba ko akasin haka aka samu cikin wadannan shekaru 25? Shirin Daga Laraba na wannan mako ya tattauna kan wannan cikar Najeriya shekara 25 cikin mulkin dimokradiyya.

Duration:00:28:52

Ask host to enable sharing for playback control

Abin Da Ke Sa Fararen Hula Su Raina Sojoji

5/22/2024
Mu’amalar farar hula da sojoji a Najeriya ta mutuntuwa ce wadda zarar aka hangi soja a cikin gari jiki har karkarwa yake. Sai dai a ‘yan kwanakin nan a iya cewa yadda labarai ke yawan fita game da yadda fararen hula ke yin tsaurin ido wajen takalar sojoji da fada yana karuwa. Shirin Daga Laraba na wannan mako ya duba abin da ya sa fararen hula ke kokarin daga hannunsu kan jami’an tsaro musamman na soji.

Duration:00:23:12

Ask host to enable sharing for playback control

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mai Aikin Hajji

5/15/2024
Yau Laraba rukunin farko na maniyyata Hajjin bana daga Najeriya za su tashi zuwa kasa mai tsarki Duk da matsin tattalin arziki da ake ciki a kasar nan, akalla mutum sama da 50,000 ne ake sa ran za su sauke faralin daga Najeriya. Shin wane abu maniyyatan ya kamata su maida hankali a kai? NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Masu Gidajen Haya Suke Tsuga KudiDAGA LARABA: Dalilan Da Za A Hana ’yan kasa da shekara 18 shiga jami’aShirin Daga Laraba na wannan mako yana dauke da amsohin wadannan bayanai game maniyyata Hajjin bana.

Duration:00:29:49

Ask host to enable sharing for playback control

Dalilin Da Za A Hana ’Yan Ƙasa Da Shekara 18 Shiga Jami’a

5/8/2024
Idan aka zagaya jami’o’i ana samun dalibai da dama wadanda ba su wuce shekara 15 ba a aji. A yanzu zamani ya sauya, abin ya zama Ruwan dare. Mai yiwuwa a lokacin da kuke makarantar firamare ko sakandare kun hadu da wadanda aka yiwa tsallaken aji, wato a bai wa dan aji 4 damar rubuta jarabawar kammala firamare ko kuma dan SS2 damar rubuta WAEC ya wuce jami’a Wannan ne ya sa gwamnatin tarayya ta ce za a tabbatar da dokar hana duk wanda bai kai shekara 18 ba zuwa matakin gaba da sakandare. Shirin Daga Laraba na wannan makon ya yi duba a kan wannan lamari.

Duration:00:23:35

Ask host to enable sharing for playback control

Muna Rayuwa A Cikin Ƙunci - Ma’aikatan Najeriya

5/1/2024
Yau ce ranar 1 ga watan Mayu da aka ware a Najeriya da wasu sassan duniya domin jinjina ga rawar da ma’aikata ke takawa wajen ci gaban kasa. Sai dai yayin da 'yan Najeriya da dama ke kuka da halin da aka shiga na ƙuncin rayuwa, ma'aikata na kan gaba wajen bayyana yadda suka ce suna tagayyara kuma aikin ba riba ta wani ɓangaren. Shirin Daga Laraba na wannan makon ya duba yadda rayuwar ma'aikata a Najeriya ke kasancewa da sauyin da ake fatan samu.

Duration:00:25:50

Ask host to enable sharing for playback control

Me Ya Sa Kamfanonin Lantarki Suke Fifita ‘Yan ‘Band A’?

4/17/2024
Bayan komawa tsarin rukuni daban-daban na bayar da wutar lantarki Idan kamfanoni na neman afuwa to yawancin ga ‘yan rukunin farko ne. Wasu na ji a ransu kamar su ba kwastomomi bane ga kamfanonin domin kulawar da ake ba su ta nuna ba a tare da su. Shirin Daga Laraba na wannan mako ya duba abin da ya sa hankalin kamfanonin wutar lantarki ya karkata wani fanni.

Duration:00:25:53

Ask host to enable sharing for playback control

Yadda Sabbin Ma'aurata Ke Morewa A Ramadan

4/3/2024
A watan Ramadan sabbin ma'aurata na alfahari da azuminsu na farko a gidan aure. Shin mene ne abin da yake kayatar da gidan aure musamman a wannan lokaci na Ramadan? Ya ya kamata ma'aurata su kasance? Shirin Daga Laraba na wannan mako ya tattauna yadda ma'aurata ke samun tabarruki da falala a yanayinsu na farko.

Duration:00:22:30

Ask host to enable sharing for playback control

Abubuwan Da Ba A So Mai I'itikafi Ya Aikata

3/27/2024
I’itikafi sunna ce mai karfi a wannan lokaci, kuma jama’a masu sukunin shiga na kwashe kwanaki kusan goma a masallaci wajen ibada. To amma me ya kamata ku sani gameda shiga itikafi kuma wadanne abubuwa ake son mutum ya kiyaye a lokacin? Shirin Daga Laraba na wannan mako ya duba matakan yin i'itikafi da abubuwan da ya kamata ku sani gameda hakan.

Duration:00:23:16

Ask host to enable sharing for playback control

Abin Da Ake Yi A Goman Tsakiyar Ramadan A Addini Da Al'ada

3/20/2024
A yayin da ake shiga goman tsakiya na watan Ramadan, malamai na kira ga al’umma da su dage wajen ibadu domin samun dacewa. A al’adance a wannan goma ta tsakiya akwai wasu al’adu musamman na tashe da kuma kirarin goma ta wuya bayan ta marmari. Shirin Daga Laraba ya yi tsokaci ne a kan wasu abubuwa da da ake yi a goman tsakiyar Ramadan a addinance da al'adance.

Duration:00:29:19

Ask host to enable sharing for playback control

Abin Da Addini Yace Game Da Azumin Ƙananan Yara

3/13/2024
Watan ramadana na jefa shauki a zukatun yara masu tasowa ta yadda har rige-rige ake tsakanin juna na ganin an kai wannan munzali. Shin ta wace hanya ya kamata iyaye su bi domin koya wa yarasu azumin ramadana? Shirin Najeriya a Yau ya duba matakan koyawa yara azumin ramadana cikin sauki.

Duration:00:22:20

Ask host to enable sharing for playback control

'Amfani Da Tsaffin Takardun Naira Zai Iya Jefa Mutum A Matsala'

3/6/2024
Mutane da dama sun shaida cewa takardar Nairar Najeriya na saurin lalacewa. Wasu na ganin masu liki a wajen bukukuwa da yadda ake kasuwancin sabbin kudi na taka rawa. Toh amma me ya kamata a yi, me kuma doka tace kan kudin da suka tsufa suka lalace. Shirin Daga Laraba na wannan mako ya duba halin da mutum zai iya jefa kansa idan har aka same shi da wulakanta takardun Naira da yadda za a bada gudummuwa wajen inganta kudin.

Duration:00:24:26

Ask host to enable sharing for playback control

"Ruwan 'Fiyowata' Na Neman Ya Gagari Talaka"

2/28/2024
Tsadar rayuwa ta sa ruwan leda wato 'fiyowata' ya fara zama abin tattaunawa gameda yadda yake tsada. Wasu na ganin shine ruwan da ake samu mai dama-dama wajen tsafta idan mutum na so ya sha ruwa, sai dai yadda yake kara tsada a sassa daban-daban na Najeriya ya sa ana komawa shan ruwa mara tsafta a wasu wuraren. Sai dai masu sarrafa ruwan na cewa ba daga su ba ne, inda har ta kai ga wasu na rufe kamfanoninsu. Shirin Daga Laraba na wannan mako ya duba dalilin da suka jawo hakan.

Duration:00:22:01