
Najeriya a Yau
News & Politics Podcasts
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Location:
Nigeria
Genres:
News & Politics Podcasts
Description:
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Twitter:
@aminiyatrust
Language:
Hausa
Contact:
09138933390
Website:
https://aminiya.dailytrust.com/
Email:
online@dailytrust.com
Episodes
Sabbin Dabarun Hana Matasa Aikata Laifuffuka
4/18/2025
Send us a text
Masu iya magana kan ce banza ba ta kai zomo kasuwa.
Mai yiwuwa hakan ne ya sa matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka shiga ofishin ’yan sanda, su kuma fita ba tare da wani ya harare su ba, balle ya kama su.
’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da kwacen waya da fyade kai har ma da satar mutane don kudin fansa a tsakanin matasa.
Ko yaya wannan dabara take aiki?
Wannan ne abin da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Duration:00:25:36
Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?
4/17/2025
Send us a text
Doctor Zainab Muhammad na daya daga cikin mata a Arewacin Najeriya da ta jajirce tare da kudirin cika burinta na karantar kimiyya duk da kalubalen da wasu matan dake yankin Arewa suke bayyanawa suna fuskanta wurin karantar fannin.
Doctor Zainab ba kimiyya kawai ta karanta ba, ta karanci daya daga cikin kimiyyoyin da ake ganin sun fi kowanne wahala wanda a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba har da mazan ma na kauracewa wannan karatun.
Zainab Kwararriyar likita ce wacce ta shahara wurin kula da marasa lafiya a asibitoci.
Duration:00:30:00
Dalilan Rikice – Rikice A Jihar Filato
4/15/2025
Send us a text
A yanzu haka, al’ummar jihar Filato na cikin fargaba da tashin hankali sakamakon jerin hare-haren da suka afku a wasu sassan jihar, inda daruruwan mutane suka rasa rayukansu, wasu kuma suka tsere daga muhallansu.
Ko mene ne dalilin sake fitowar rikice-rikicen da suka dabaibaye yankin da ake ganin an fara samun zaman lafiya?
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan rikice rikicen Jihar Filato da dalilan aukuwar su.
Duration:00:26:09
Dalilan "Farfaɗowar Boko Haram" A Jihar Borno
4/14/2025
Send us a text
A yanzu haka al’ummar Borno na cikin zulumi sakamakon wasu hare-haren da ake zargin kungiyar Boko Haram ce ta kai a wasu sassan jihar.
Wadannan hare-hare dai suna faruwa ne bayan shekaru da dama da ikirarin Gwamnati na cewa an yi nasarar nakasa kungiyar.
Ko mene ne dalilin sake farfadowar kungiyar ta Boko Haram a wannan lokaci?
Wannan ne batun shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Duration:00:30:48
Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar 'Yan Najeriya
4/11/2025
Send us a text
A Najeriya ana tafka muhawara a kan yadda farashin danyen man fetur yake kara faduwa a kasuwannin duniya.
Wannan lamari dai ya haddasa damuwa a zukatan wasu ’yan Najeriya, kama daga masana tattalin arziki zuwa ga jami’an gwamnati, kasancewar danyen mai ne mafi muhimmanci a cikin hanyoyin samun kudin shiga.
Sai dai tambayar da wasu ’yan kasa suke yi ita ce: shin yaya wannan faduwa ta farashin danyen mai za ta shafi rayuwar talakan Najeriya?
Duration:00:27:58
Tasirin Da Dangantakar Yan Uwa Yake Ga Rayuwar Alumma
4/10/2025
Send us a text
Irin dangantakar dake kasancewa tsakanin abokai na da matukar tasiri ga farin cikin wadannan abokai, ta yadda a wasu lokutan ma baka iya banbancewa tsakanin ‘yan uwan su na jini da kuma abokai.
Irin wannan dangantaka ya kamata ne ace ana samun shi a wurin wadanda suke uwa daya uba daya ko kuma wadanda suke uba daya.
Sai dai a yayin da wasu ke samun kyakkyawan dangantaka tsakanin su da yan uwan su na jini, wasu kuwa basa ga maciji tsakanin su da nasu ‘yan uwan da suke uwa daya uba daya.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan irin tasirin da 'yan uwantaka ke dashi ga rayuwar mutum.
Duration:00:20:50
Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu
4/8/2025
Send us a text
A zamanin yau, ba kira da tura saƙo kawai ake yi da wayar hannu ba; baya ga haka, muhimmiyar hanya ce ta samun kuɗi da bunƙasa sana’o’i.
Ko kun san dabarun amfani da wayoyinku don samun kuɗaɗen shiga?
Idan ba ku sani ba, ko kuma kuna buƙatar ƙarin sani, ku biyo mu a shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci.
Duration:00:24:01
Menene Tasirin NYSC Bayan Shekaru 50 Da Kafa Shi?
4/7/2025
Send us a text
Shirin bautar ƙasa wanda aka kafa tun a shekarar 1973, an kirkire shi da nufin haɗa kan matasa daga kowane lungu da saƙo na ƙasar nan, domin fahimtar juna da kawar da wariyar yanki da kabilanci.
Amma a yau, bayan shekaru fiye da arba'in da biyar da fara wannan shiri, jama’a da dama na tambaya:
ko har yanzu shirin na da tasirin da aka kirkire shi domin shi?
Ko har yanzu bautar ƙasa NYSC na ci gaba da samar da haɗin kai da ake buƙata a Najeriya?
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan ko har yanzu kwalliya na biyan kudin sabulu kan kafa shirin bautar kasa?
Duration:00:25:06
Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
4/4/2025
Send us a text
Cututtuka da dama suna Kamari a Najeriya wanda a mafi yawancin lokuta ma wadanda ke dauke da irin wadannan cututtukan basu da masaniyar suna dauke da su.
Kamar yadda majalisar dinkin duniya ta bayyana, zaman lafiya, rashin matsalar kwakwalwa, da samun wadata na daga cikin abubuwan dake tabbatar da lafiyar bil’adama.
Wata cuta da ta addabi da yawa daga cikin al’umma itace cutar Hawan jini wacce take daya daga cututtuakan dake sanadiyyar mutuwar akalla mutum miliyan biyu a duk shekara a Najeriya.
Duration:00:24:51
Kalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyan 'Ya'yan Su
4/3/2025
Send us a text
Duk wanda ya shekara arbain zuwa sama ya san irin tarbiyyan da ya samo daga wurin iyayen sa a da baya can, irin mu’amalan dake tsakanin sa da iyaye har ma da shakuwan dake tsakanin ‘ya’ya da iyaye.
A yanzu kuwa abubuwa sun canza daga yadda aka san su, inda abubuwa suka rincabe sukayi wa iyaye yawa.
Daya daga cikin manyan sauyin da aka samu sun hada da aikin gwamnati ko aikin wata da iyaye mata suke yi a wannan zamani wanda hakan a wasu lokuta ke barazana ga irin kulawan da ‘ya’ya suke samu.
Shirin Najeriya A Yau zai yi Nazari ne kan irin kalubalen da iyaye ke fuskanta a wannan zamani wajen tarbiyyan ‘ya’yan su.
Duration:00:27:12
Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
4/1/2025
Send us a text
Alqurani mai girma a cikin suratul Baqarah Allah ya wajabta wa musulmi da suka cika wasu sharudda azumtar watan Ramadana.
Kamar yadda malamai suka sha fadi, wannan wata na dauke da wasu falala maras misaltuwa da bawa kan samu idan ya maida kai wajen ibada don samun rabauta daga ubangiji.
Kazalika hadisai sun ruwaito kan falalar azumtar kwanaki shidda na watan shawwal, watan dake biye da Ramadan.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan falalar dake akwai ga wanda ya azumci kwanaki shidda na watan shawwal.
Duration:00:24:06
Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
3/31/2025
Send us a text
Watan azumin ramadana kan zo da sauye sauye da dama da suka hada da kara kaimi wajen bauta wa ubangiji, samun lada ta hanyar ciyar da alumma da kuma falala masu yawa da basu misaltuwa.
Wani sauyi da watan azumin watan ramadana ke zuwa dashi shine canjin yanayin ciman alumma, inda mutane ke canzawa daga cin abinci sau uku ko sama da haka a rana zuwa sahur da kuma bude baki.
Bayan kwanaki 29 zuwa talatin na samun wadannan canji, ta wadanne hanyoyi ne alumma zasu koma cimaka kamar yadda suka saba gabanin watan ramadana?
Shirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan hanyoyin da mutum ya kamata yabi don komawa cin abinci yadda ya kamata bayan azumtar watan Ramadana.
Duration:00:24:02
Abubuwan Da Ya Kamata Musulmi Su Yi Gabani Da Ranar Sallah
3/28/2025
Send us a text
Lokutan sallah kamar yadda aka sani lokacin ne na farin ciki, nuna godiya ga ni’imar da Allah yayi mana da kuma bauta.
Kazalika lokacin ne da zamu lura da tabbatar da aiyukan da zamu aikata su zama ingattattu.
Ko wadanne irin abubuwa ne mutane ya kamata su aikata kafin da kuma ranar sallah?
Wadanne hanyoyi za a bi don tabbatar da zaman lafiya yayin gudanar da bikin sallah?
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi Nazari ne kan abubuwan da musulmi ya kamata suyi gabani da kuma ranar sallah.
Duration:00:27:32
Halin Da Matasa Suka Tsinci Kan Su A Najeriya
3/27/2025
Send us a text
Yau a Najeriya da yawa daga cikin matasa na fuskantar kalubale musamman wajen biya ma kan su bukatun su na yau da kullum sakamakon yanayin tattalin arzikin kasa, rashin aikin yi da kuma tsadar rayuwa.
A wasu lokutan irin wadannan matasa sun yi karatu, wasu ma na da sana’oin su na hannu amma rashin aiki mai gwabi da zai biya musu bukatun su na cigaba da yin barazana da irin halin da suke tsintar kan su a ciki.
Wannan matsayi da matasan kasar nan suka tsinci kansu a ciki na cigaba da tura su cikin kuncin rayuwa.
Shirin Najeriya A Yau na wanna rana zai yi Nazari ne kan irin kalubalen rayuwa da matasan kasar nan ke tsintar kan su a ciki musamman a farko farkon rayuwar su.
Duration:00:24:45
Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Kasa Kiranye
3/25/2025
Send us a text
Mulkin demokradiyya kamar yadda Hausawa ke cewa ‘yancin dan adam.
A lokacin da ta baka damar tsayawa don a zabe ka kan wani mukami, kazalika ta baka damar zaben wanda kake so ya shugabance ka kuma ya wakilce ka.
Wani abun da demokradiyyar ta baiwa alumma dama a kai kuma shine na yin kiranye ga wakilan da suka zaba musamman idan wadannan wakilan basa biya musu bukatun da suka tura su a kai.
Tuni dai alummar kogi ta tsakiya suka fara kada kuri’un kiranye ga sanatar da suka aike ga majalisar dattawa bisa dalilai nasu na kashin kan su.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai tattauna ne kan matakai da sharuddan da ake cikawa don yin kiranye ga ‘yan majalisa.
Duration:00:30:12
Yadda Kasuwanci Ke Kasancewa Gabani Da Cikin Ramadana
3/24/2025
Send us a text
Hausawa sunyi gaskiya da suka ce ‘yawan mutane sune kasuwa’.
Yawan hada hadar da ake yi tsakanin ‘yan kasuwa da abokan cinikin su na daya daga cikin abun da zai tabbatar maka kasuwanci na gudana kamar yadda ake so.
Sai dai da Zarar ance watan Ramadana ya kama wasu daga cikin kasuwanci kan samu nakasu, inda wasu kuma ke samun habbaka.
Wasu kuwa kasuwar ce ke sauya salo, inda take dakushewa a wasu sa’anni ta kuma habbaka a wasu sa’anni.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan yadda wasu kasuwanci ke habbaka da kuma yadda wasu ke samun koma baya cikin watan Azumin Ramadana.
Duration:00:22:17
Illar Sare Itatuwa Ga Canjin Yanayi Da Lafiyar Mu
3/21/2025
Send us a text
Shekaru da dama kenan da hukumomin duniya ke gudanar da tarurruka da dama kan zakulo hanyoyin da za a kawo karshen dumamar yanayi a duniya.
Dumama ko canjin yanayi na cigaba da barazana ga duniya, inda ake samun sauye sauye ga yanayi da wasu abubuwa da masana ke bayyana ka iya kara ta’azzara in ba’ayi wani abu a kai ba.
Daya daga cikin abubuwan da masana suka bayyana dake kawo wannan matsala itace yadda alumma ke kada itatuwan da aka dasa ba tare da lura da illar da hakan ke jawowa ga muhalli ba.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi Nazari ne kan illar sare itatuwa ba tare da dasa wasu ba kan sauyin yanayi da kuma lafiyar mu.
Duration:00:30:13
Dalilan Da Ke Hana Wasu Teloli Cika Alƙawari
3/20/2025
Send us a text
Sana’a na taka muhimmiyar rawa wajen habbaka tattalin arzikin alumma.
Alumma da dama musamman a wannan lokacin na kara bayyana alfanun koyan sana’ar hannu don dogaro da kai maimakon dogara da aikin gwamnati ko na kamfani.
Sai dai ana zargin wasu masu sana’ar hannu da rashin cika alkawari a wurin sana’ar su.
Irin wadannan masu sana’ar hannun teloli na daga cikin su, wadanda a mafi yawan lokuta ake zargin su da rashin cika alkawari musamman a lokutan bukukuwa na musamman.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi Nazari ne kan dalilan da suka sa telolin basa cika alkawari.
Duration:00:23:03
Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan
3/18/2025
Send us a text
Mallakan Muhalli na daya daga cikin burin kowanne dan Najeriya.
Sai dai wannan buri a mafi yawan lokacin baya cika musamman ga masu matsakaitan samu.
Kananan ma’aikata da mafi karancin albashin su yake naira dubu saba’in ba zai ciyar dasu, ko tufatar dasu ba, ballantana har suyi tunanin mallakan muhalli nasu na kashin kansu.
Sai dai masana na bayyana cewa marasa karfin ma na iya mallakan nasu muhallin daidai ruwa daidai tsaki.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi Nazari ne kan hanyoyin da mai karamin karfi zai bi don mallakan muhalli a Najeriya.
Duration:00:27:23
Guraben Ayyukan Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya
3/17/2025
Send us a text
Duk da kukan rashin aikin yi da ako da yaushe ke cigaba da addabar ‘yan Najeriya, a wasu lokutan ba rashin aikin yi ne matsalar ba, wadanda zasu cike guraben ayyukan ne suka yi karanci a Najeriya.
Alkaluma na cigaba da bayyana dubban ‘yan Najeriya ne dai ke fito wa daga manyan makarantun kasar a kowace shekara.
A yayin da da yawa basa samun aikin yi, so tari akwai dimbin guraben ayyuka da babu masu cike su don babu kwararrun da ake bukata.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai tattauna ne kan guraben ayyukan da aka kasa cike su da kuma nemo hanyoyi don magance matsalar.
Duration:00:23:50