Najeriya a Yau-logo

Najeriya a Yau

News & Politics Podcasts

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

Location:

Nigeria

Description:

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

Language:

Hausa

Contact:

09138933390


Episodes

Wa Ya Kamata Ka Sa A Matsayin Magajinka?

9/26/2023
Kowane mutum na fatan ganin ya samu magaji amintacce wanda ba zai iya cin amanar sa ba, musamman wajen cike wasu takardu a rayuwa. Wasu mutanen kan saka matansu ko 'ya'ya ko miji. Amma akwai masu fargabar hakan kuskure ne saboda komai na iya faruwa. A shrin Najeriya a Yau mun yi nazari a kan mutumin da ya kamata a riƙa sakawa a matsayin magaji.

Duration:00:14:14

“Yadda Na Sayar Da Gado Na Na Yi Karatu”

9/25/2023
Alkaluma da ke bayyana binciken da ake yawan yi kan wadanda basa zuwa makaranta musamman a Arewacin Najeriya na nuna cewa mata ne suka fi yawa a cikin wadan da basa zuwa karatu. Mene ne ke hana mata da dama karatu a Arewacin Najeriya? Shirin Najeriya A Yau na tafe da bayanai daga bakin ‘yan mata, da matan da suka samun damar yin karatu, da kuma shawarwarin yadda za a magance matsalolin. Domin sauke shirin kai tsaye, latsa nan.

Duration:00:14:16

Wane Mataki Za A Ɗauka Kan Cin Zarafi Da Kisan ‘Yan Jarida

9/22/2023
A duk lokacin da ake wani al’amari da jama’a ke bukatar masaniya a kai, ‘yan jarida na sahun gaba wajen ganin sun kutsa domin samun rahotanni. Sai dai a lokuta da dama a kan samu cikas daga wasu jami’an tsaro da a ko da yaushe kokarin su shine hana ‘yan jarida shiga wasu wurare musamman idan abun ya shafi manyan jami’an gwamnati. A gefe guda kuma, wasu ‘yan jaridan na gamuwa da ajalinsu a bakin aiki. Shirin Najeriya a Yau ya duba matakan da ya kamata a dauka gameda cin zarafin ‘yan jarida da kisan gilla da ake ma wasu.

Duration:00:15:36

Me Zai Faru Bayan Hukuncin Kotu Kan Zaɓen Kano

9/21/2023
Za a iya bakin aƙalami ya bushe a tashin farko na matakin kujerar gwamna a jihar Kano. An gudanar da shari'ar da ta baiwa Nasiru Gawuna na jam'iyar APC nasa a kan gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf a wani salo na zamani da wasu basu taɓa gani ba. Shirin Najeriya a Yau ya duba me zai iya faruwa bayan wannan hukuncin.

Duration:00:14:58

Shin Matasa Sun Gamsu Da Ministocin Da Ake Son Naɗa Musu?

9/19/2023
An bayyana sunan matasa sabbin jini har mutum 2 da ake son naɗawa a muƙamin ministocin ma’aikatar matasa ta Najeriya. Yawanci an saba ma’aikatar matasa akan haɗe ta da ta wasanni a damƙawa mutum guda, sai gashi a wannan karon an yi ƙarami da babbar mnistan matasa, kuma dukansu ba wanda ya haura shekara 35. To ko yanzu za a iya cewa waɗannan matasa da za a naɗa zai gamsar sabbin jini a Najeriya? Ku saurari cikakken shirin

Duration:00:14:54

Yadda 'Yan Kasuwa Ke Neman Hana Kayan Abinci Sauka

9/18/2023
Rahotanni daga wadansu jihohin Najeriya na bayyana cewa farashin kayan abincin ya sauka a kasuwanni, sakamakon fara shigowar kaka, sai dai a wadansu jihohin kuma kamar Katsina farashin hawa ya ke. Ko mene ne dalilin karuwar farashin kayan masarufi a wadansu kasuwannin? Shirin Najeriya A Yau ya bankado gaskiyar dalilan da farashin kayan abincin ke hauhawa duk da shigowar kaka. Domin sauke shirin kai tsaye, latsa nan.

Duration:00:14:58

Wa Zai Kula Da Motocin Sufurin Da Zulum Ya Kawo?

9/15/2023
Gwamnatin jihar Borno karkashin jagorancin Farfesa Babagana Umara Zulum ya kaddamar da motocin sufuri a kwaryar birnin jihar, domin rage radadin cire tallafin man fetur din da aka yi a Kasar nan. Shin ta wadanne hanyoyi za a bi domin kula da wadannan motoci? Shirin Najeriya A Yau ya ji ta bakin jamaar Borno, ya kuma bi diddigin hanyoyin da gwamnatin za ta bi wurin kula da motocin.

Duration:00:14:23

Yadda Matsin Tattalin Arziki Ke Shafar Karatu A Najeriya

9/14/2023
A yayin da aka dawo karatu a makarantun Firamare da Sakandare a wadansu sassan Najeriya a farkon wannan makon. Ko a wane irin hali iyayen yara su ka tsinci kan su? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya zanta da iyayen, ya kuma ji ta bakin wani mai makaranta domin sanin yadda matsin tattalin arziki ke shafar dawowar yara makaranta.

Duration:00:14:26

Dalilin Da Ake Yawan Samun Hatsarin Jirgin Ruwa A Neja

9/12/2023
Daga watan Agustan 2023 zuwa yanzu, an samu hatsarin jirgin ruwa sau 3 a Jihar Neja wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutane da dama, da kuma dukiya mai tarin yawa. Shin mene ne ke janyo yawaitar hatsarin jirgin ruwan? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci na tafe da karin bayani. Latsa nan domin sauke shirin kai tsaye.

Duration:00:13:02

"Hanyoyi 5 Da Sarakunan Gargajiya Za Su Kawo Karshen Taadanci"

9/11/2023
Kungiyar gwamnonin Arewa Maso Gabashin Najeriya ta bayyana cewa akwai sarakunan gargajiya da ke sauke baki ba tare da bincike ba, wadanda wasu kan rikide zuwa yan ta'adda. Ko mene ne abin da ya kamata a yi domin magance gurbacewar al'umma? Shirin Najeriya A Yau ya ji ta bakin sarakunan gargajiya, ya kuma ji ta bakin wani masanin tsaro domin gano bakin zaren.

Duration:00:14:21

Abin Da Ya Bambanta Sheikh Giro Argungu Sauran Malamai

9/8/2023
Rasuwar Sheikh Abubakar Giro Argungu sakamakon rashin lafiya a daren shekaranjiya Laraba 6 ga Satumba, ta ruda mutane da dama, a Najeriya da kuma makwabta. Ko mene ne ya banbanta Sheikh Abubakar Giro Argungu da sauran al'umma? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci na tafe da bayanai game marigayin, daga bakin makusantansa.

Duration:00:14:49

Abin Da Ya Bambanta Kotun Zaɓen 2023 Da Na Baya

9/7/2023
Abubuwa da dama sun faru a kotun sauraren ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasa a zaman ta na jiya. An yi fatali da wasu ƙararrakin yayin da jam'iyyu ke ta nuna bara'a da hukuncin. A shirin Najeriya a Yau, mun duba abin da ya bambanta zaman kotun da kuma hukunce-hukuncen da aka yi waɗanda suka sha bamban da na shekarun baya da aka saba yi

Duration:00:14:37

Dalilin Rufe Kasuwannin Dabbobi 8 A Jihar Zamfara

9/5/2023
A kokarin magance kalubalen tsaro dake addabar jihar Zamafara, gwamnatin jihar ta ce a rufe dukkanin wasu kasuwannin dabbobi a jihar. Hakan ya biyo bayan korafe korafen da ake na cewa ana yawan kai dabbobin sata a irin wadannan kasuwanni. To amma meyasa aka maida hankali a kasuwannin dabbobi kadai? abin da shirin mu na Najeriya a yau ya maida hankali kenan.

Duration:00:13:23

‘Har Yanzu Ba Wacce Aka Tabbatar Ta Sume Bayan Yi Mata Sallama’

9/4/2023
Jita-jita ta karade kafafen sada zumunta cewa wadansu mata suna zuwa gidajen jama'a da zarar sun yi sallama an amsa sai wanda ya amsa ya sume. Shin da gaske ne akwai wanda a ka taba yi wa sallama ta sume? Shirin Najeriya A Yau ya ziyarci jihohin Najeriya hudu domin binciko gaskiyar labarin.

Duration:00:14:24

Yadda Bawali A Waje Ke Yada Cututtuka

9/1/2023
Mutane da dama na fakewa da sun matsu su rika yin bawali a kan titi, ko gefen wuraren shakatawa. Ko kun san irin cututtukan da yin bawali a fili ke janyowa? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci na tafe da karin bayani.

Duration:00:14:56

Mece ce Makomar Kwankwaso A Siyasar Najeriya?

8/31/2023
Batun dakatarwar da jam’iyyar NNPP ta yi wa dan takararta na Shugaban Kasa a zaben 2023, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na daya daga cikin batutuwan da ke daukar hankalin ’yan siyasa a Najeriya. Shin da gaske ne wannan takalar hancin makomar Kwankwaso ne a siyasar Najeriya? Shirin Najeriya A Yau ya doki jaki ya doki taiki. A yi sauraro lafiya.

Duration:00:13:55

Yadda Masu Son Fara Ƙananan Sana’o’i Ke Wahala Wajen Yin Rajista

8/29/2023
Masu son fara ƙananan sana'o'i kan fuskanci kalubale da dama a lokacin suke yunƙurin ganin sun tsaya da kafafun su, musamman gameda batun rijista da samun haƙƙin mallaka a wasu matakan. Irin waɗannan matakai ne ke sa mutum ya iya cin gajiyar wani abu idan ya taso da ke buƙatar sai an cika wasu sharuɗɗa. Sai dai ba kasafai ake samun iya cika ƙa'idojin cikin sauki ba. Shirin Najeriya a yau ya yi nazari akan yadda masu son fara sana'o'i ke shan wahala domin cika matakan da ake buƙata

Duration:00:13:59

Yadda Bude Madatsar Lagdo A Kamaru Zai Shafi 'Yan Najeriya

8/28/2023
Hukumar kula da Harkokin Kasashen Waje Ta Najeriya ta aikewa Hukumar Bada Agajin Gaggawa NEMA sakon Kasar Kamaru na niyyar bude madatsar ruwan Lagdo, sakamakon cikar da madatsar ya yi. A bara bude wannan madatsa ya raba 'yan Najeriya sama da Miliyan guda da matsugunansu, ko ta wadanne bangarori wannan ruwa zai shafi Najeriya bana? Shirin Najeriya A Yau na tafe da karin bayani.

Duration:00:13:49

Shin Tinubu Zai Naɗa Ɗansa Ministan Matasa?

8/25/2023
A daidai lokacin da aka zura ido domin ganin wanda za a naɗa ministan matasa, tuni shugabannin matasan APC suka cimma matsaya a kan shugaban ƙasa Tinubu ya naɗa ɗan sa a wannnan kujera. Sai dai kawunan matasan ya rabu, sakamakon yadda suka ce mulki ba abin da za a maida shi na 'yan uwa da iyali ba ne. Shirin Najeriya A Yau ya maida hankali kan yadda matasa ke ta kara-kai-na gameda kujerar ministan matasa.

Duration:00:14:55

Yadda Ministoci Ke Gasar Burge Tinubu

8/24/2023
Tun bayan da aka rantsar da ministocin gwamnatin Tinubu, kowannen su ke ta shan alwashin cimma wani muradi ga 'yan Najeriya. Wasu ganin akwai alƙawuran da za a iya siffanta su da romon-baka, amma ba lallai su cika ba. A cikin shirin Najeriya a Yau, mun duba hanyoyin da ministocin za su bi domin ganin sun baiwa maraɗa kunya a kan alƙawuran da suka ɗauka.

Duration:00:14:08